fidelitybank

Kotu za ta fara sauraron karar Abba da Gawuna ranar Alhamis

Date:

Kotun Ƙolin Najeriya ta sanya ranar Alhamis, 21 ga watan Disamba domin sauraron ƙarar da aka shigar kan zaɓen gwamnan jihar Kano.

Gwamna Kabir Abba Yusuf na jam’iyyar NNPP na kalubalantar hukuncin kotun daukaka ƙara da ta tabbatar da hukuncin kotun sauraran ƙararrakin zaɓe da ta soke nasararsa tare da bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar na ranar 11 ga Maris.

Lauyan Gwamna Yusuf, Barista Bashir Tudun Wazirci, ya tabbatar wa BBC cewa an ba su sanarwar fara sauraron ƙarar a matsayinsu na tawagar lauyoyin da ke wakiltar gwamnan da jam’iyyarsa.

Wannan ne karon farko da kotun za ta fara zama, inda za ta fara jin bahasi, yayin da har yanzu akwai muhimman takardun da ba a kai wa kotun ba.

“Har yanzu akwai takardun da muka [NNPP] ba su [APC] da ba su dawo mana da martani ba tukunna, kuma mu ma muna da damar sake yin martani idan suka dawo da su,” in ji Bashir Tudun Wazirci.

Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukuncin cewa Gwamna Yusuf ba dan jam’iyyar NNPP ba ne a lokacin da ya tsaya takarar gwamna.

Amma tabbataccen kwafin hukuncin, wanda ya bayyana kwanaki kaɗan bayan zaman kotun, ya kunshi bayanai masu karo da juna game da hukuncin da ya janyo ce-ce-ku-ce.

Duka ɓangarorin biyu dai sun yi iƙirarin cewa hukuncin ya tabbatar da nasarar da suka samu a zaben.

Sai dai jam’iyyar NNPP ta shigar da ƙara a gaban kotun ƙoli, inda take ƙalubalantar hukuncin kotun daukaka ƙara da ta tabbatar da hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaben gwamna.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp