fidelitybank

Kotu za ta duba yuwar bayar da belin Yahaya Bello

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello tare da wasu mutane biyu da Hukumar EFCC ta gurfanar a gaban kotu a yau Laraba sun musanta zarge-zargen rashawa na Naira biliyan 80 da ake yi musu.

Yahaya Bello, wanda shi ne na farko a cikin mutanen da ake tuhuma tare da sauran mutanen biyu Shuaibu Oricha da Abdulsalami Hudu, sun musanta duka tuhuma 16 da aka fara karanto musu a gaban mai shari’a Maryanne Anenih ta babbar kotun ta Abuja.

Joseph Daudu, (SAN – babban lauya) shi ne jagoran lauyoyin da ke kare toshon gwamnan da sauran waÉ—anda ake tuhuma, yayin da Kemi Pinhero (shi ma babban lauya – SAN), ke jagorantar masu gabatar da Æ™ara.

Bayan musanta aikata laifukan, lauyan waÉ—anda ake tuhumar ya nemi a bayar da belin Bello amma lauyan EFCC ya nemi kada a bayar da cewa wa’adi ya wuce tun watan Oktoba.

To amma bayan sauraron ɓangarorin biyu kotun ta tsayar da ranar 10 ga watan Disamba mai kamawa domin duba buƙatar belin.

EFCC ta yi nasarar gurfanar da tsohon gwamnan na jihar ta Kogi a gaban kotun ta tarayya da ke Abuja a yau Laraba bayan wata da watanni na gaza hakan, kasancewar ya ƙi amsa gayyatar hukumar kuma duk yunƙurinta na kama shi ya ci tura.

A jiya Talata ne aka ce tsohon gwamnan ya kai kanshi hukumar ta EFCC da rakiyar lauyoyinsa – amma daga baya hukumar ta ce tana tsare da shi.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi É—an shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin Æ´an Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp