fidelitybank

Kotu ta yi watsi da buƙatar Emefiele a dawo masa da gidajen da EFCC ta ƙwace

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Najeriya ta yi watsi da buƙatar tsohon gwamnan Babban Bankin Najeriya CBN, Godwin Emefiele, ta neman a dawo masa da rukunin gidajen da gwamnati ta ƙwace.

A ranar 2 ga watan Disamba ne hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta samu amincewar kotu domin ƙwace unguwa guda mallakar Mista Emefiele da ke Abuja babban birnin ƙasar.

Unguwar da ke yankin Lokogoma ta ƙunshi gidaje 753.

Tsohon gwamnan ya nemi kotun ta ƙara masa lokaci domin gabatar da buƙatar neman jingine umarnin da ta bayar na ƙwace rukunin gidajen a watan Disamban 2024.

Ya yi iƙirarin cewa bai san lokacin da kotun ta yanke hukuncin ƙwace gidajen ba, sannan ya zargi EFCC da wallafa sanarwar neman mamallakin gidajen a wani “ɓoyayyen sashe na shafin jarida ta yadda zai yi wahala ya iya rubuta martani a kan lokaci”.

Sai dai Mai Shari’a Jude Onwuegbuzie ya yi watsi da iƙirarin nasa, yana mai cewa sanarwar da aka wallafa a rabin shafin jarida ta ƙasa ya wadatar.

legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp