fidelitybank

Kotu ta yi watsi da bukatar biyan Igboho Naira biliyan 20

Date:

Kotun daukaka kara ta yi watsi da bukatar biyan Sunday Igboho naira biliyan 20 saboda asarar da ya yi a gidansa.

Da yake yanke hukunci a karar da babban attoni janar na kasa da hukumar kula da tsaron farin kaya da daraktan hukumar a jihar Oyo suka shigar a kan hukuncin mai shari’a Muslim Hassan na babbar Kotun Jihar Oyo ya yanke na cewa hukuncin da mai shari’a Ladiran Akintola, ya yanke na cewa a biya Igboho kudin ya sabawa ka’ida.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa a ran 17 ga watan Satumban 2021, mai shari’a Akintola ya bukaci a biya Igboho naira biliyan 20 a matsayin kudin asarar kayaki da ya yi a gidansa bayan hari da ya yi zargi ‘yan bindiga suka kai masa ranar 1 ga watan Yuli wadda kuma ya sabawa umurnin babban attoni janar na kasa, Abubakar Malami da kuma hukumar tsaron farin kaya da suka kalubalanci hukuncin.

Mai shari’a Hassan ya ce babu wasu hujjoji da suka marawa hukuncin babbar kotun jihar ta Oyo.

Ya ce mai shari’a Akintola bai gano asarar da Igbohon ya ce ya yi ba a tsawon bincikensa, inda ya kara da cewa babu kwararan hujjoji da suka nuna yawan asarar da Igbohon ya yi a gidansa.

Mai shari’a Hassan ya kuma kara da cewa ba wata hujja ko bincike da ta nuna mutum biyu sun mutu yayin hari a gidan dan gwagwarmayar kamar yadda ya yi ikirari.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp