fidelitybank

Kotu ta yi watsi da bukatar biyan Igboho Naira biliyan 20

Date:

Kotun daukaka kara ta yi watsi da bukatar biyan Sunday Igboho naira biliyan 20 saboda asarar da ya yi a gidansa.

Da yake yanke hukunci a karar da babban attoni janar na kasa da hukumar kula da tsaron farin kaya da daraktan hukumar a jihar Oyo suka shigar a kan hukuncin mai shari’a Muslim Hassan na babbar Kotun Jihar Oyo ya yanke na cewa hukuncin da mai shari’a Ladiran Akintola, ya yanke na cewa a biya Igboho kudin ya sabawa ka’ida.

Jaridar The Nation ta ruwaito cewa a ran 17 ga watan Satumban 2021, mai shari’a Akintola ya bukaci a biya Igboho naira biliyan 20 a matsayin kudin asarar kayaki da ya yi a gidansa bayan hari da ya yi zargi ‘yan bindiga suka kai masa ranar 1 ga watan Yuli wadda kuma ya sabawa umurnin babban attoni janar na kasa, Abubakar Malami da kuma hukumar tsaron farin kaya da suka kalubalanci hukuncin.

Mai shari’a Hassan ya ce babu wasu hujjoji da suka marawa hukuncin babbar kotun jihar ta Oyo.

Ya ce mai shari’a Akintola bai gano asarar da Igbohon ya ce ya yi ba a tsawon bincikensa, inda ya kara da cewa babu kwararan hujjoji da suka nuna yawan asarar da Igbohon ya yi a gidansa.

Mai shari’a Hassan ya kuma kara da cewa ba wata hujja ko bincike da ta nuna mutum biyu sun mutu yayin hari a gidan dan gwagwarmayar kamar yadda ya yi ikirari.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...

Gwamnati za ta gina titin jirgi a jihohi shida

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta haɗa gwiwa da...

Tinubu ya na cikin koshin lafiya – Farouk Adamu Aliyu

Tsohon ɗan majalisar wakilai daga jihar Jigawa, Faruk Adamu...

Amurka ta saka ladan dala miliyan biyar a kamo jagoran ‘yandaban Haiti

Amurka ta sanya dala miliyan biyar a matsayin lada...

Gwamnati ta janye karar da ta shigar kan Fasinjar jirgin Ibom

Gwamnatin Tarayya ta janye ƙarar da ta shigar kan...

Na so komawa Manchester United a 2012 – Lwandowski

Ɗanwasan gaban ƙungiyar Barcelona ta Spain, Robert Lewandowski ya...

Isak ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gaba Alexander Isak ya nace sai ya bar...

Sadiq Umar da Bello El-Rufai sun sayi ƙungiyar Ranchers Bees ta Kaduna

Ɗanwasan tawagar Super Eagles ta Najeriya da Real Socieded...

Atiku zai iya guduwa daga ADC ya koma PDP idan Jonathan ya tsaya takara – Diran

Tsohon mataimakin sakataren yada labaran jam’iyyar PDP na kasa,...

Zoben matar Ronaldo ya kai dala miliyan 5 – Masana

Masana sun yi kiyasin tsadar zoben da Cristiano Ronaldo...

Kama Tambuwal ya na da alaka da shigarsa cikin hadakar jam’iyya – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ce kama...
X whatsapp