fidelitybank

Kotu ta yi watsi da belin jami’in Binance

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Abuja babban birnin Najeriya ta yi watsi da buƙatar bayar da belin jami’in kamfanin kuɗin kirifto na Binance, Tigran Gambaryan wanda ya shafe fiye da kwana 40 a tsare a gidan yarin Kuje da birnin tarayyar.

Yayin da yake gabatar da hukuncin, mai shari’a Emeka Nwite ya ce ya yi nazarin takardar neman belin da aka gabatar masa, sai dai ya ce akwai yiwar mista Gambaryan zai iya tserewa idan aka bayar da belinsa.

Hukumar EFCC ce gurfanar da jami’in tare da abokin aikinsa Nadeem Anjarwalla, da kuma kamfanin Binance a gaban kotun bisa zarge-zarge biyar masu alaƙa da almundahanar kuɗi da ya kai kimanin dala miliyan 35.4 a shafin kamfanin.

Hama ma hukumar tara haraji ta ƙasar, FIRS na zargin mutanen uku da laifuka hudu da suka jiɓanci ƙin biyan haraji.

Waɗanda ake zargin dai sun musanta duka zarge-zargen.

An dai fara shari’ar ta yau ne kan almundahanar kuɗi, ta hanayr gabatar da shaida daga hukumar kula da hannayen jari ta ƙasar.

A makon da ya gabata ne dai shugaban kamfanin na Binance, Richard Teng ya zargi wasu jami’an gwamnatin Najeriya da neman a ba su cin hancin dala miliyan 150, domin kashe maganar.

Zargin da hukumomin ƙasar suka musanta, suna masu bayyana shi da ”ɓata suna” da kuma kawar da hankalin mutane kan shari’ar da ke gudana.

Kawo yanzu dai ba a san inda Nadeem Anjarwalla yake ba bayan tserewarsa daga hannun hukumomin Najeriya.

To sai dai hukumomin ƙasar sun ce suna aiki da jami’an ‘yan sandan ƙasa da ƙasa, a wani mataki na samun sammacin ƙasa da ƙasa a ƙasa domin kama shi a duk inda yake.

daily post news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp