fidelitybank

Kotu ta yi fatali da dan takarar Sanatan APC

Date:

Wata babbar kotu da ke Yola a jihar Adamawa, ta kori Elisha Abbo a matsayin dan takarar Sanatan Adamawa ta Arewa a zabe mai zuwa.

Kotun ta kuma hana jam’iyyar All Progressives Congress (APC) amincewa da shi a haka.

Mai shari’a Danladi Mohammed ne ya yanke hukuncin a ranar Litinin. Mai shari’a Danladi ya yanke hukuncin cewa Sanata Abbo bai cancanci sake tsayawa takara ba tunda jam’iyyar ta kore shi.

Alkalin ya kuma bayyana cewa Sanatan da jam’iyyar APC na da nasaba da kudurin shugabannin kananan hukumomin Mubi ta Arewa na jam’iyyar mai kwanan wata 7 ga watan Oktoba 2022, wanda ya kori dan majalisar; don haka bai cancanci ya ci wani hakki ko wata gata da aka ba ‘yan APC ba.

Sannan ya bukaci Sanata Abbo da ya daina bayyana kansa a matsayin dan takarar jam’iyyar na shiyyar.

A halin da ake ciki, Sanatan da ke cikin rudani ya caccaki hukuncin, inda ya bayyana shi a matsayin hukuncin daurin talala.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp