fidelitybank

Kotu ta yi fatali da bukatar Abba Kyari

Date:

Babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yi watsi da buƙatar da tsohon shugaban sashen tattara bayanan sirri na rundunar ‘yan sandan Najeriya Abba Kyari ya gabatar a gabanta, yana neman kotun ta yi watsi da zarge-zargen da ake yi masa.

Yayin zaman kotuna a ranar Laraba alƙalin kotun mai shari’a Emeka Nwite ya yi watsi da buƙatar Abba Kyari, yana mai cewa kotun na da hurumin sauraron ƙararrakin da suke da alaƙa da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi kamar yadda kundin tsarin mulki da dokar da ta kafa hukumar NDLEA suka ba ta dama.

Abba Kyari ya faɗa wa kotun cewa hukumar NDLEA ta yi gaggawar gabatar da shi a gaban kotu, tun kafin a kammala bincike, yana mai cewa kamata ya yi hukumar ta bai wa ‘yan sanda damar gudanar da binciken cikin gida, kafin ita NDLEA ta ɗauki mataki.

Ya ƙara da cewa ‘yan sanda sun gudanar da bincike kan lamarin kuma har sun gabatar da rahoton cikin gida ga rundunar ‘yan sanda.

Jami’in ‘yan sanda ya ce za a gabatar da shi a gaban kotu ne kaɗai, idan ‘yan sanda suka kammala gudanar da bincike.

Ya kuma ce dokar aikin ‘yan sanda ta ce hukumar kula da ayyukan ‘yan sanda ta ƙasar na da ikon da za ta gudanar da bincike tare da ladabtar da jami’an ‘yan sanda, kamar yadda majalisar ƙoli ta ayyukan shari’a ke da ikon ladabtar da ma’aikatan shari’a.

To sai dai alƙalin kotun ya ce ikon da hukumar kula da ayyukan ‘yan sandan ke da shi , bai zarta ikon da kotun tarayyar ke da shi ba.

Kyari mai muƙamin mataimakin kwamshinan ‘yan sanda, tare da wasu mutum huɗu da ke aiki a rundana ɗaya na fuskantar tuhume-tuhumen haɗin baki wajen safarar hodar ibilis da nauyinta ya kai kilogiram 17.55

legit nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp