Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Talata, ta yi barazanar yin watsi da karar da DCP Abba Kyari da aka dakatar, ya shigar da hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA.
Mai shari’a Inyang Ekwo, ta ba da wannan gargadin ne biyo bayan jinkirin da lauya Kyari, Cynthia Ikena, ta yi, na yiwa lauyan NDLEA, Joseph Sunday, karin tabbacinta bayan an ba ta takardar shaidar tun ranar 28 ga watan Fabrairu.
A zaman da aka ci gaba da sauraren karar a ranar Lahadi, wani darakta mai kula da kararraki da shari’a na hukumar, ya sanar da cewa, Ikena ya mika masa kara ne kawai a safiyar yau. In ji Guradian.
Lauyan ya bayar da hujjar cewa, ta hanyar tsari na 2 na Dokokin Hakkokin Bil Adama, 2019, mai nema bai samu lokacin shigar da bukatar ba.
Ikena, wadda ta yi korafin cewa, ta yi kokarin ganawa da Kyari a tsare hukumar ta NDLEA kimanin guda uku amma aka hana ta, ta yi addu’ar Allah ya ba ta lokaci domin ta daidaita takardar.
Mai shari’a Ekwo, a wani takaitaccen hukunci da ya yanke, ya yi barazanar soke karar idan lauyan bai shirya ba a kwana mai zuwa.
Alkalin kotun ya dage sauraron karar zuwa ranar 7 ga watan Afrilu domin sauraren karar.