Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan mutumin, Oluwatimileyin Ajayi da ya kashe budurwarsa Salome Adaidu hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa samunsa da laifin kisa.
Mai shari’a Simon Aboki ne ya jagoranci zaman kotun kuma ya yanke hukuncin a yau, ranar Alhamis.
Kotun ta same shi da laifin kashe da kuma fille kan Salome Adaidu.
An gurfanar da Ajayi bisa tuhuma ɗaya ta kisan kai da gangan, wanda ya saɓa da Sashe na 221 na Dokar Penal ta Arewacin Najeriya, wadda take ɗauke da hukuncin kisa.
Timileyin Ajayi ya musanta laifin aikata kisan a gaban kotu lokacin da sauraron shari’ar ya fara.
A ranar 12 ga watan Janairun 2025 ne dai Jami’an tsaro suka damƙe saurayin, wanda mawaƙin yabo na addinin kirista ne, ɗauke da kan Salome, kusa da wani coci.