Wani alkali ya yanke wa tsohon shugaban hukumar leken asiri ta Gambia, da wasu jami’an tsaro hudu hukuncin kisa, saboda kisan wani mai gwagwarmayar dumukuradiyya a 2016, daidai karshen gwamnatin tsohon Shugaba Yahya Jammeh.
A lokacin an kama, Ebrima Solo Sandeng – wanda jigo ne a jam’iyyar hamayya ta United Democratic Party, yayin wata zanga-zanga ta kin jinin gwamnati.
Kwana biyu bayan kama dan siyasar, ya mutu a gidan yari, sakamakon duka da azabtarwa da aka yi masa.
Mutuwar tasa ta kara harzuka jama’a, abin da a karshe ya kai ga ganin bayan Shugaba Jammeh bayan shekara 22 a kan mulki. In ji BBC.
Yanya Jammeh ya tsere zuwa Equatorial Guinea, a 2017, inda har yanzu yake zaman gudun-hijira.