An yanke wa wani kanal ɗin soja a Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo hukuncin kisa, saboda samun sa da hannu a kisan masu zanga-zanga sama da 50 a watan Agusta.
Jami’an soja da ke aiki karkashin kanal ɗin mai suna Mike Mikombe, sun buɗe wuta kan mambobin wata ƙungiyar addini lokacin da suke zanga-zangar da aka haramta don nuna adawarsu da dakarun wanzar da zaman lafiya na MDD a birnin Goma da ke gabashin ƙasar.
An zarge shi da laifin take ƴancin dan adam.
Wata kotun soji ta kuma samu wasu sojoji uku da aikata laifuka, inda ta yanke musu hukuncin ɗaurin shekara goma a gidan yari.
Lauyoyin kanal Mikombe sun ce za su ɗaukaka ƙara.
An dai sha yanke hukuncin kisa a Kongo, amma rabon da a zartas da hukuncin kisa a kan wani, ya kai shekara sama da shekara 20.