Mai shari’a Inyang Ekwo na babbar kotun tarayya a Abuja, ya yi fatali da tuhumar halasta kuɗin haram da hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa arzikin ƙasa zagon ƙasa take yi wa tsohon atoni janar na kasa, Mohammed Adoke.
Gidan talabijin na Channels ya ruwaito cewa da yake yanke hukunci kan ƙarar da tsohon babban jami’in ya shigar ta neman a soke ƙarar, alƙali Ekwo ya ce EFCC ta gaza gabata da shaida kan Adoke.
EFCC ta tuhumi Adoke da Abubakar Aliyu, wani mai harkar gine-gine a 2017, da almundahana da naira miliyan 300.
Alƙali Ekwo ya kori ƙarar tare da wanke shi.
Sai dai Ekwo ya yanke cewa Aliyu Abubakar, mutum na biyu da ake ƙara, dole ya nemi shaida saboda akwai zarge-zargen da ya kamata ya kare kansa.