Wata kotu a Nairobi ta umurci matuƙa jirgin saman Kenyan Airways su koma bakin aiki da ƙarfe shida na safen ranar Laraba, kuma su dakatar da yajin aikin da suka kwashe kwana huɗu suna yi.
Matuƙa jiragen saman sun shiga yajin aiki ne domin nuna adawa da matakin kamfanin jiragen na dakatar da kason da yake bayarwa ga asusun tara kuɗaɗen murabus na ma’aikata.
Mai shari’a Anna Ngubuini Mwaure ta umurci matuƙan su koma bakin aiki har sai idan wata kotun ta yanke wani hukuncin da ya inganta matakin yajin aikin.
Ta kuma yanke hukuncin cewar kamfanin jiragen saman ya ƙyale matuƙa jiragen su yi ayyukansu ba tare da tsangwama ba.
Kamfanin dai ya ce yajin aikin na janyo masa hasarar kuɗi dala miliyan biyu da rabi a kowace rana.