fidelitybank

Kotu ta umarci INEC ta tsige sunan mataimakin dan takarar Gwamnan LP

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta ba da umarnin cire sunan Idu Onyiloyi, mataimakin dan takarar gwamnan jihar Benuwe a karkashin jam’iyyar Labour Party (LP) daga jerin sunayen hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).

Mai shari’a Inyang Ekwo, a wani hukunci da ya yanke ranar Laraba, ya kuma dakatar da Onyiloyi daga ci gaba da bayyana kansa a matsayin mataimakin dan takarar gwamna na jam’iyyar LP a zaben ranar Asabar, bayan da ya janye takararsa da kan sa.

Ku tuna cewa Dr Ochechi Adejor ya kai karar LP, INEC da Onyiloyi a matsayin wadanda ake kara na daya zuwa na uku.

Karanta Wannan: Obi ya jagoranci tawagar Lauyoyinsa zuwa kotu

Adejor ya nemi umarnin tilastawa INEC buga sunansa a matsayin mataimakin dan takarar gwamna na LP a zaben Benue.

Sai dai da yake yanke hukuncin a yau, Mai shari’a Ekwo ya ce ya gano cewa shaidun mai kara (Adejor) a shari’ar gaskiya ce.

Ya ce, “Na gano cewa mai gabatar da kara ya tabbatar da karar ta da sahihiyar hujjoji kuma yana da hakkin yanke masa hukunci kuma na rike.”

Alkalin, ya bayyana cewa Adejor shi ne dan takarar mataimakin gwamnan jihar LP a zaben jihar Benuwe, bayan da aka tsayar da shi a matsayin dan takara mai inganci bayan ficewar Onyiloyi da son rai.

Ya kuma ba da umarnin dakatar da INEC daga ci gaba da buga ko karbar sunan Onyiloyi ko kuma wani mutum wanda ba Adejor ba a matsayin dan takarar da ke wakiltar LP a ofishin mataimakin gwamnan Benue a babban zaben bana.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp