Wata babbar kotun tarayya da ke zaman ta a Umuahia, jihar Abia, ta umarci Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC), da ta biya wata ‘yar jarida da ke Umuahia, Norah Okafor Naira miliyan 3.5.
Kotun ta yi Allah-wadai da hukuncin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta yi wa mai shigar da kara ba bisa ka’ida ba a karshen sa’o’i 23 ga Satumba, 2021.
Kotun karkashin jagorancin mai shari’a Thomas Johnson, ta kuma umarci hukumar EFCC da ta gabatar da uzuri a cikin jaridu guda biyu na kasa ga wanda abin ya shafa.
Idan za a iya tunawa, a ranar 23 ga Satumba, 2021 ne jami’an hukumar yaki da cin hanci da rashawa suka mamaye gidan ‘yar jaridar da ke Umuahia, bayan da suka yi zargin lalata shinge, kofofinta da sauran kayanta.
An ce jami’an na EFCC na ci gaba da gudanar da bincike, domin gano wasu da ake zargi da damfarar ta internet.