fidelitybank

Kotu ta tsayar da ranar yanke wa Malam Abduljabbar hukunci

Date:

Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kano ta saka ranar 15 ga watan Disamban 2022, domin yanke hukunci kan tuhume-tuhumen da ake yi wa malamin nan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.

Gwamnatin Kano na tuhumar shehin malamin da yin ɓatanci ga Annabin Musulunci Muhammadu S.A.W. kuma an tsare shi tun daga watan Yulin 2021.

Abduljabbar zai sake bayyana a gaban Mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola na kotun da ke Ƙofar Kudu ne bayan ƙungiyar lauyoyi masu bai wa marasa gata kariya ta ce bai cancanci su ba shi kariyar ba saboda yana samun fiye da naira N30,000 duk wata.

An nemi a ba shi kariyar ce sakamakon lauya Ambali Muhammad ya fice daga kariyar da yake bai wa Abduljabbar a shari’ar a watan Yuni da ya gabata.

Kafin tsare shi, Abduljabbar ya yi iƙirarin cewa kare Annabin yake yi maimakon ɓatanci kamar yadda ake zargin sa, abin da ya sa gwamnatin Kano ta shirya muƙabala tsakaninsa da wasu malamai a jihar.

Alƙalin muƙabalar ya yanke hukuncin cewa Abduljabbar bai amsa tambayoyi da ƙalubalen da aka yi masa ba game da kalaman da yake yi kan Manzon Allah a lokacin muhawarar kamar sauran takwarorinsa.

Sai dai malamin, wanda ɗa ne ga shahararren jagoran ɗariƙar Ƙadiriyya Malam Nasiru Kabara, ya yi zargin rashin adalci daga masu shirya muƙabalar kuma ya nemi a sake shirya wata daban, abin da gwamnatin ta yi watsi da shi.

An gudanar da muƙabalar bayan malamin ya gabatar da karauka daban-daban yana mai neman a zauna muhawarar.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp