fidelitybank

Kotu ta tsayar da ranar yanke wa Malam Abduljabbar hukunci

Date:

Kotun Shari’ar Musulunci da ke Kano ta saka ranar 15 ga watan Disamban 2022, domin yanke hukunci kan tuhume-tuhumen da ake yi wa malamin nan Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.

Gwamnatin Kano na tuhumar shehin malamin da yin ɓatanci ga Annabin Musulunci Muhammadu S.A.W. kuma an tsare shi tun daga watan Yulin 2021.

Abduljabbar zai sake bayyana a gaban Mai Shari’a Ibrahim Sarki Yola na kotun da ke Ƙofar Kudu ne bayan ƙungiyar lauyoyi masu bai wa marasa gata kariya ta ce bai cancanci su ba shi kariyar ba saboda yana samun fiye da naira N30,000 duk wata.

An nemi a ba shi kariyar ce sakamakon lauya Ambali Muhammad ya fice daga kariyar da yake bai wa Abduljabbar a shari’ar a watan Yuni da ya gabata.

Kafin tsare shi, Abduljabbar ya yi iƙirarin cewa kare Annabin yake yi maimakon ɓatanci kamar yadda ake zargin sa, abin da ya sa gwamnatin Kano ta shirya muƙabala tsakaninsa da wasu malamai a jihar.

Alƙalin muƙabalar ya yanke hukuncin cewa Abduljabbar bai amsa tambayoyi da ƙalubalen da aka yi masa ba game da kalaman da yake yi kan Manzon Allah a lokacin muhawarar kamar sauran takwarorinsa.

Sai dai malamin, wanda ɗa ne ga shahararren jagoran ɗariƙar Ƙadiriyya Malam Nasiru Kabara, ya yi zargin rashin adalci daga masu shirya muƙabalar kuma ya nemi a sake shirya wata daban, abin da gwamnatin ta yi watsi da shi.

An gudanar da muƙabalar bayan malamin ya gabatar da karauka daban-daban yana mai neman a zauna muhawarar.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...

Jami’ar Bayero ta Kano ta yi sabon shugaba

Farfesa Haruna Musa, ya karɓi ragamar shugabancin jami’ar Bayero...

Gwamnatin Kano ta amince Barau FC ta yi wasa a filin Sani Abacha

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da kungiyar kwallon kafa...

Gwamnatin Tinubu na takalar Kwankwaso da fada – Buba Galadima

Jigo a jam'iyyar NNPP, kuma na hannun tsohon gwamnan...

Newcastle United ta dauki dan wasan tsakiya Jacob daga Aston Villa

Newcastle United ta sanar da daukar dan wasan tsakiya...
X whatsapp