Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 10 ga watan Mayu domin ci gaba da sauraren karar da ke neman a dakatar da zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar PDP a ranar 28 ga watan Mayu.
Wani dan takarar shugaban kasa, Mista Cosmas Ndukwe, ya shigar da karar tsohon jam’iyyar na neman umarnin hana jam’iyyar PDP ci gaba da zaben fidda gwani da aka shirya gudanarwa.
Lokacin da aka kira lamarin jiya, lauyan mai kara, Mista Paul Erokoro (SAN), ya shaida wa kotun cewa ya samu takardar shaidar PDP da ke nuna dalilin da ya sa ba za a dakatar da zaben fidda gwani ba a ranar Laraba.
Erokoro ya roki kotun da ta dage shari’ar domin ya samu damar duba takardar tare da amsa dalilan da PDP ta kawo kan karar wanda yake karewa.