Wata kotun shari’a da ke zamanta a unguwar Hausawa Filin Hockey a cikin birnin Kano, ta bayar da umarnin tsare wata shahararriyar mai magana a shafin sada zumunta TikTok, Murja Ibrahim Kunya, a gidan gyaran hali.
A ranar Alhamis din nan ne aka gurfanar da ita a gaban kuliya bisa tuhumar da ake mata na bata suna, rashin mutunci, dagula al’umma da kuma tauye zaman lafiyar jama’a.
An kara zargin bata suna ne a kan karar da wasu Tik Tokers biyu: Aisha Najamu da Idris Maiwushirya suka shigar, inda suka zargi Murja da bata sunan su.
Karanta Wannan: ‘Yan sanda sun cafke Murja ‘yar Tik Tok a Kano
Bayan da lauya mai shigar da kara, Lamido Sorondinki ya karanta wa wadanda ake tuhumar duka tuhume-tuhumen, ta musanta aikata laifin.
Bayan haka, lauyan Murja, Yasir Musa ya gabatar da bukatar neman belin ta, amma lauyan masu gabatar da kara ya ki amincewa da shi.
Alkalin kotun, Abdullahi Halliru, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake tuhuma a gidan yari sannan ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Fabrairu domin yanke hukunci kan neman belin.
Ku tuna cewa a kwanakin baya ‘yan sanda sun kama Murja a Kano bisa umarnin wata kotun Shari’a.