fidelitybank

Kotu ta tsare Murja ‘yar TikTok a gidan gyaran halin Kano

Date:

Wata kotun shari’a da ke zamanta a unguwar Hausawa Filin Hockey a cikin birnin Kano, ta bayar da umarnin tsare wata shahararriyar mai magana a shafin sada zumunta TikTok, Murja Ibrahim Kunya, a gidan gyaran hali.

A ranar Alhamis din nan ne aka gurfanar da ita a gaban kuliya bisa tuhumar da ake mata na bata suna, rashin mutunci, dagula al’umma da kuma tauye zaman lafiyar jama’a.

An kara zargin bata suna ne a kan karar da wasu Tik Tokers biyu: Aisha Najamu da Idris Maiwushirya suka shigar, inda suka zargi Murja da bata sunan su.

Karanta Wannan: ‘Yan sanda sun cafke Murja ‘yar Tik Tok a Kano

Bayan da lauya mai shigar da kara, Lamido Sorondinki ya karanta wa wadanda ake tuhumar duka tuhume-tuhumen, ta musanta aikata laifin.

Bayan haka, lauyan Murja, Yasir Musa ya gabatar da bukatar neman belin ta, amma lauyan masu gabatar da kara ya ki amincewa da shi.

Alkalin kotun, Abdullahi Halliru, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake tuhuma a gidan yari sannan ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Fabrairu domin yanke hukunci kan neman belin.

Ku tuna cewa a kwanakin baya ‘yan sanda sun kama Murja a Kano bisa umarnin wata kotun Shari’a.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp