fidelitybank

Kotu ta tsare Murja ‘yar TikTok a gidan gyaran halin Kano

Date:

Wata kotun shari’a da ke zamanta a unguwar Hausawa Filin Hockey a cikin birnin Kano, ta bayar da umarnin tsare wata shahararriyar mai magana a shafin sada zumunta TikTok, Murja Ibrahim Kunya, a gidan gyaran hali.

A ranar Alhamis din nan ne aka gurfanar da ita a gaban kuliya bisa tuhumar da ake mata na bata suna, rashin mutunci, dagula al’umma da kuma tauye zaman lafiyar jama’a.

An kara zargin bata suna ne a kan karar da wasu Tik Tokers biyu: Aisha Najamu da Idris Maiwushirya suka shigar, inda suka zargi Murja da bata sunan su.

Karanta Wannan: ‘Yan sanda sun cafke Murja ‘yar Tik Tok a Kano

Bayan da lauya mai shigar da kara, Lamido Sorondinki ya karanta wa wadanda ake tuhumar duka tuhume-tuhumen, ta musanta aikata laifin.

Bayan haka, lauyan Murja, Yasir Musa ya gabatar da bukatar neman belin ta, amma lauyan masu gabatar da kara ya ki amincewa da shi.

Alkalin kotun, Abdullahi Halliru, ya bayar da umarnin a ci gaba da tsare wanda ake tuhuma a gidan yari sannan ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 16 ga watan Fabrairu domin yanke hukunci kan neman belin.

Ku tuna cewa a kwanakin baya ‘yan sanda sun kama Murja a Kano bisa umarnin wata kotun Shari’a.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp