fidelitybank

Kotu ta tsare matashin da ya yi wa ‘yar shekara 7 fyade

Date:

Wata kotun Majistare da ke Kaduna ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 27 mai suna Musa Haruna a gidan gyaran hali, bisa zarginsa da yunkurin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 9 fyade.

Alkalin kotun, Ibrahim Emmanuel, wanda bai amsa rokon Haruna ba na rashin hurumin sauraron karar ya umarci ‘yan sanda da su mayar da fayil din karar zuwa ga daraktan kararrakin jama’a na jihar Kaduna domin samun shawarar lauya.

Sai dai ya dage ci gaba da sauraron karar zuwa ranar 30 ga watan Satumba.

Ana tuhumar Haruna da ke zaune a Ungwan Rimi Kaduna da yunkurin fyade.

Mai gabatar da kara, Insp. Chidi Leo, ya shaidawa kotun cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne a ranar 2 ga watan Satumba a gidansa.

Leo ya ce wanda ake tuhumar ya yaudari yarinyar mai shekaru 9 a cikin dakinsa kuma ya yi yunkurin yi mata fyade.

Mai gabatar da kara ya kara da cewa kukan yarinyar ya sanar da wasu makwabta da suka kubutar da ita tare da mika wanda ake tuhuma ga ‘yan sanda.

Laifin a cewarsa ya sabawa tanadin sashe na 207 na dokar jihar Kaduna ta shekarar 2017 (kamar yadda aka gyara).

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp