fidelitybank

Kotu ta tirsasa ‘yan Yahoo su uku yi wa mutanen Abuja aikin hidima

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta yanke wa wasu barayin shafin internet uku, wadanda aka fi sani da ‘yahoo boys’ hukuncin yiwa al’umma hidima.

Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, reshen Abuja shiyyar Abuja, ta gurfanar da yaran uku a gaban kuliya bisa laifin zamba.

A wata sanarwa da hukumar ta EFCC ta fitar a ranar Talata, ta bayyana sunayen mutanen uku da suka hada da: Victor Joseph, Mohammed Edogi Mohammed da Johnson Nifemi.

Karanta Wannan: ‘Yan Yahoo sun kwashe kudin Kwastam sama da Naira miliya 523

An yanke musu hukunci ne a ranar Litinin bayan an gurfanar da su a kan tuhume-tuhume guda daya da kowanne ke damun su kan zamba ta intanet.

A cewar sanarwar, ana zargin Joseph da yin kamar shi injiniyan ruwa ne mai suna Zhang Li, inda ya samu N150,000 daga wani Xiao dan kasar China.

Mohammed, wanda ake zargi na biyu, shi ma ya buga sunan Bryan Alex a wasu manhajojin sada zumunta na zamani, ya kuma samu N1,500,000 daga hannun Lekin Elli, Williana da Flavio; da Nifemi, wanda ake zargi na uku, ya bayyana a matsayin injiniyan Amurka mai suna John Alpha, ya kuma damfari Jane Appado, ‘yar kasar Amurka dala $170.

Babban Kotun FCT dake Gwagwalada, karkashin Mai shari’a A.I. Akobi, ya yanke hukuncin ne na aikin yi wa al’umma hidima bayan samun wadanda ake zargin da aikata laifin.

Sanarwar ta bayyana cewa, “An zargi Joseph da yin kame-kame a matsayin injiniyan ruwa mai suna Zhang Li, inda ya samu Naira 150,000 (Naira Dubu Dari da Hamsin Kadai) daga wani Xiao, dan kasar China, yayin da Mohammed kuma ya fito a matsayin Bryan Alex a shafukan sada zumunta daban-daban. apps kuma sun sami N1,500,000 (Miliyan Daya Dubu Dari Biyar Kadai) daga LekinElli, Williana da Flavio. Nifemi ya kwaikwayi wani injiniya dan kasar Amurka John Alpha sannan ya damfari wata Jane Appado ‘yar kasar Amurka dalar Amurka $170 (Dalar Amurka dari da saba’in).”

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp