fidelitybank

Kotu ta tirsasa matar da ta yiwa makarantar ɗan ta rashin kunya yin sharar dole na wata 6

Date:

Wata kotun majistare da ke zamanta a yankin Ota a jihar Ogun ta umarci wata mata mai suna, Biola Joshua, mai shekaru 43 da ta share harabar makarantar sakandare ta Iju-Ebiye na tsawon watanni shida.

Rundunar ‘yan sandan ta tuhumi Miss. Joshua da laifin hada baki, cin zarafi da kuma rashin zaman lafiya, bayan ta kutsa kai cikin makarantar da danta ke karatu da ‘yan daba.


Mai shigar da kara na ‘yan sanda, Cynthia Ejezie, ta ce, Joshua, da danta da sauran su, a ranar 11 ga Maris, 2021, da misalin karfe 2:00 na rana, sun mamaye ofishin shugaban makarantar da na jami’in lafiya na makarantar, ya kuma yi musu rauni a jiki.

A hukuncin da ta yanke, Alkalin Kotun Mai shari’a Shotunde Shotayo ya yankewa matar hukuncin tare da umarce ta da rika share makarantar daga karfe 8:00 na safe zuwa 11:00 na safe kowace rana na tsawon watanni shida.

Alkalin kotun ya ba da umarnin cewa, makarantar ta bude littafi ga mai laifin, inda za a rika rubuta ayyukanta na yau da kullum.

Shotayo, ya ba ta zabin biyan tarar Naira dubu 30,000.

nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...
X whatsapp