fidelitybank

Kotu ta taƙa wa tsagin Gwamnan Bauchi na tsige shugaban PDP

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Zamfara ta ki amincewa da bukatar wani bangare mai goyon bayan shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP, Gwamna Bala Mohammed na gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa (NEC).

Kungiyar ta garzaya kotu domin ta ba da umarnin gudanar da taron na NEC yayin da rikicin bangaran jam’iyyar ya kara ruruwa.

Da yake yanke hukunci kan karar, Mai shari’a Salim Ibrahim ya ki amincewa da bukatar.

Wani bangare na jam’iyyar PDP a karkashin jagorancin gwamnan Bauchi Bala Mohammed, sun tunkari kotu suna neman a ba su umarnin gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa (NEC).

A baya dai wasu gwamnonin da aka zaba a jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Mohammed sun yi yunkurin tsige shugaban riko na kasa Amb. Umar Damagum.

Matakin ya kara dagula rikicin cikin jam’iyyar, yayin da wasu masu ruwa da tsaki musamman masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike suka nuna adawa da matakin.

Ita ma babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin hana jam’iyyar cire Damagum.

An shigar da karar bangaren Mohammed ne a babbar kotun tarayya da ke jihar Zamfara.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp