Kotun Kolin Najeriya ta tabbatar da Sanata Muhammad Adamu Aliero a matsayin ɗan takarar kujerar sanata ta Kebbi ta tsakiya a ƙarkashin inuwar jam’iyyar PDP.
A ranar Litinin ne tawagar alƙalan kotun biyar ƙarƙashin jagorancin mai shari’a China Centus Nweze, suka yi watsi da hukuncin kotun ɗaukaka ƙara da na babbar kotun tarayya suka yanke a baya, a kan zaɓen fitar da gwani da jam’iyyar ta gudanar.
Alƙalan sun yanke hukuncin cewa ƙalubalantar ayyana Saidu Haruna a matsayin ɗan takarar sanata a jam’iyyar PDP yana kan daidai.
Haka kuma kotun ƙolin ta tabbatar da zaɓen Dakta Abubakar Yahaya Abdullahi a matsayin ɗan takarar sanatan Kebbi ta arewa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP.
A yanzu Sanata Aliero – wanda tsohon gwamnan jihar Kebbi ne – zai fafata da gwamnan jihar mai ci Atiku Bagudu, wanda ke takarar kujerar sanatan a jam’iyyar APC mai mulkin jihar.