fidelitybank

Kotu ta tabbatar da takarar Gwamnan Ebonyi Umahi

Date:

Kotun Ƙolin ta tabbatar wa Gwamnan Ebonyi Dave Umahi, takararsa ta kujerar sanata da yake yi a babban zaɓen 2023 mai zuwa.

Cikin wani matakin bai-ɗaya da suka yanke, rukunin alƙali biyar na kotun ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Kudirat Ekekere-Ekun sun kori ƙarar da mai adawa da takarar tasa Princess Ann Agom-Eze ta shigar a ranar Juma’a.

Kafofin labarai a Najeriya sun ruwaito cewa alƙalan sun amince cewa ƙarar ba ta cancanci a saurare ta ba kuma dalilin da ya sa suka kore ta kenan.

Agom-Eze ta kai ƙarar ce da zimmar kotun ƙolin ta jingine hukunce-hukuncen da Babbar Kotun Tarayya da Kotun Ɗaukaka Ƙara suka yi na amincewa da sakamakon zaɓen da ya ayyana Umahi a matsayin wanda ya yi nasara.

Ita ce ta zo ta biyu a zaɓen da aka gudanar lokacin da aka bayyana Austin Umahi a matsayin wanda ya yi nasara, wanda ɗan uwa ne ga Gwamna Dave Umahi.

Sai dai gwamnan ya shiga takarar ce bayan kayen da ya sha a zaɓen fitar da gwani na ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC mai mulkin ƙasa, inda ƙaninsa Austin ya janye tare da ba shi tikitin takarar.

Hakan na nufin wannan ne hukunci na ƙarshe da za a yi a shari’ar.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp