fidelitybank

Kotu ta tabbatar da takarar Gwamnan Ebonyi Umahi

Date:

Kotun Ƙolin ta tabbatar wa Gwamnan Ebonyi Dave Umahi, takararsa ta kujerar sanata da yake yi a babban zaɓen 2023 mai zuwa.

Cikin wani matakin bai-ɗaya da suka yanke, rukunin alƙali biyar na kotun ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Kudirat Ekekere-Ekun sun kori ƙarar da mai adawa da takarar tasa Princess Ann Agom-Eze ta shigar a ranar Juma’a.

Kafofin labarai a Najeriya sun ruwaito cewa alƙalan sun amince cewa ƙarar ba ta cancanci a saurare ta ba kuma dalilin da ya sa suka kore ta kenan.

Agom-Eze ta kai ƙarar ce da zimmar kotun ƙolin ta jingine hukunce-hukuncen da Babbar Kotun Tarayya da Kotun Ɗaukaka Ƙara suka yi na amincewa da sakamakon zaɓen da ya ayyana Umahi a matsayin wanda ya yi nasara.

Ita ce ta zo ta biyu a zaɓen da aka gudanar lokacin da aka bayyana Austin Umahi a matsayin wanda ya yi nasara, wanda ɗan uwa ne ga Gwamna Dave Umahi.

Sai dai gwamnan ya shiga takarar ce bayan kayen da ya sha a zaɓen fitar da gwani na ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APC mai mulkin ƙasa, inda ƙaninsa Austin ya janye tare da ba shi tikitin takarar.

Hakan na nufin wannan ne hukunci na ƙarshe da za a yi a shari’ar.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
X whatsapp