fidelitybank

Kotu ta tabbatar da nasarar Idris Kawu a matsayin zaɓaɓɓen ɗan majalisa mai wakiltar Kumbotso

Date:

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta soke hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta kasa da ta jihar ta yanke kan zaben Majalisar Wakilai ta Kano na mazabar Kumbotso.

Hukuncin farko ya bayyana Mannir Babba Danagudi na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a matsayin wanda ya lashe zaben yayin da ya cire Idris Kawu na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) a matsayin zababben wakilin mazabar Kumbotso a majalisar wakilai ta tarayya.

Alkalan kotun uku karkashin jagorancin Mai shari’a Tunji Oyebamuji ne suka yanke hukunci, inda suka bayyana cewa karamar kotun ta tafka kura-kurai ta hanyar ba da fifiko kan hukuncin da aka yanke kan takardar shaidar Idris Kawu, duk da rashin gabatar da ita ga Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC).

Kotun daukaka kara ta kuma ce karamar kotun ta yi kuskure ne ta hanyar dogaro da shaidun da aka sa a gaba domin yanke hukunci.

Bugu da kari, kotun ta tabbatar da cewa Mannir Babba Danagudi ya kasa bayar da sahihin shedu da za su tabbatar da soke nasarar da Idris Dankawu ya samu a zaben mazabar tarayya ta Kumbotso.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp