Kotun sauraron ƙorafin zaɓen gwamnan a jihar Sokoto, ta tabbatar da nasarar gwamnan jihar Ahmad Aliyu.
Kotun ta kori karar da ɗan takarar jam’iyyar PDP, Saidu Umar ya shigar, inda yake kalubalantar sakamakon zaɓen ranar 18 ga watan Maris.
Kotun ta yi watsi da karar ne saboda rashin gamsassun hujjoji.
Mai magana da yawun gwamnan jihar a Sokoto, Abubakar Bawa, ya ce sun yi farin ciki da hukuncin kotun.
“Mun godewa Allah da jam’iyyarmu da al’ummar jihar Sokoto domin zaɓar ɗan takarar mu da suka,” in ji Bawa.
Ya bayyana cewa ‘yan jam’iyyar PDP na da damar Ɗaukaka ƙara idan har ba su gamsu da hukuncin ba.
Sakataren watsa labarai na jam’iyyar PDP a jihar ta Sokoto, Hassan Sahabi, ya bayyana wa BBC cewa hukuncin ya zo mu su da ba-zata kasancewar suna da gamsassun hujjoji da suka shigar a gaban kotu.
”Akwai batun maguɗin zabe da kuma aringizon kuri’u da aka yi, akwai bayanan da muka gabatar waɗanda da an tsaya an yi nazari akan su yadda ya kamata, to da muna kyautata zaton za a yi mana adalci”.
Jam’iyyar ta PDP ta kuma nuna rashin gamsuwa da yadda aka yi watsi da karar da suka shigar game da bambancin suna da aka suke zargi a takardun ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC, Ahmad Aliyu.
Sahabi ya ce za su tattauna da lauyoyinsu domin ɗaukar mataki na gaba.