fidelitybank

Kotu ta tabbatar da nasarar gwamnan Sokoto

Date:

Kotun sauraron ƙorafin zaɓen gwamnan a jihar Sokoto, ta tabbatar da nasarar gwamnan jihar Ahmad Aliyu.

Kotun ta kori karar da ɗan takarar jam’iyyar PDP, Saidu Umar ya shigar, inda yake kalubalantar sakamakon zaɓen ranar 18 ga watan Maris.

Kotun ta yi watsi da karar ne saboda rashin gamsassun hujjoji.

Mai magana da yawun gwamnan jihar a Sokoto, Abubakar Bawa, ya ce sun yi farin ciki da hukuncin kotun.

“Mun godewa Allah da jam’iyyarmu da al’ummar jihar Sokoto domin zaɓar ɗan takarar mu da suka,” in ji Bawa.

Ya bayyana cewa ‘yan jam’iyyar PDP na da damar Ɗaukaka ƙara idan har ba su gamsu da hukuncin ba.

Sakataren watsa labarai na jam’iyyar PDP a jihar ta Sokoto, Hassan Sahabi, ya bayyana wa BBC cewa hukuncin ya zo mu su da ba-zata kasancewar suna da gamsassun hujjoji da suka shigar a gaban kotu.

”Akwai batun maguɗin zabe da kuma aringizon kuri’u da aka yi, akwai bayanan da muka gabatar waɗanda da an tsaya an yi nazari akan su yadda ya kamata, to da muna kyautata zaton za a yi mana adalci”.

Jam’iyyar ta PDP ta kuma nuna rashin gamsuwa da yadda aka yi watsi da karar da suka shigar game da bambancin suna da aka suke zargi a takardun ɗan takarar gwamna a jam’iyyar APC, Ahmad Aliyu.

Sahabi ya ce za su tattauna da lauyoyinsu domin ɗaukar mataki na gaba.

punch newspaper headlines today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp