fidelitybank

Kotu ta tabbatar da nasarar gwamnan Kebbi

Date:

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da zaben Nasir Idris a matsayin zababben gwamnan jihar Kebbi da aka yi ranar 18 ga watan Maris.

Kotun a wani hukunci da ta yanke a yammacin ranar Juma’a ta yi watsi da karar da jam’iyyar PDP da dan takararta na gwamna, Janar Aminu Bande suka shigar a gabanta saboda rashin cancantar su.

A wani hukunci na bai daya da mai shari’a Ndukwe Anyanwu ya yanke, kotun daukaka kara ta warware dukkan wasu batutuwa biyar da aka tsara domin tabbatar da gaskiya ga gwamnan da kuma jam’iyyar PDP.

Mai shari’a Anyanwu ya bayyana cewa ba a kafa tuhume-tuhume na jabun shedu da aka kai wa mataimakin gwamnan jihar, Abubakar Umar Tafida ba kamar yadda doka ta tanada.

Ta kuma kara da cewa batutuwan rashin bin tanadin dokar zabe wajen gudanar da zaben ba za su iya tsayawa ba saboda masu shigar da kara sun kasa tabbatar da yadda zarge-zargen ya shafi zaben.

Daga bisani mai shari’a Anyanwu ya tabbatar da hukuncin kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Kebbi wadda a baya ta yi watsi da karar da PDP ta shigar tare da tabbatar da zaben gwamnan.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp