fidelitybank

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Delta

Date:

Gwamnan jihar Delta Sheriff Oborevwori, ya sake samun nasara a kotun koli tare da yin watsi da karar da jam’iyyar Social Democratic Party, SDP da dan takararta na gwamna Kenneth Gbagi suka shigar kan rashin cancantar su.

A wani hukunci na bai daya da ta yanke a ranar Juma’a, kotun kolin ta yi watsi da duk wasu dalilai da zarge-zargen da aka yi kan zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga Maris din shekarar da ta gabata.

Mai shari’a Mohammed Garba Lawal, wanda ya yanke hukuncin, ya ce zargin da ake yi na cewa jam’iyyar PDP, dan takararta, Oborevwori, bai cancanci zaben ba abin dariya ne domin babu wata shaida da ta tabbatar da zargin.

Mai shari’a Lawal ya yi watsi da ikirarin cewa zaben bai inganta ba, kuma ba a yi zaben gwamna da mafi rinjayen kuri’un da aka kada a zaben ba.

A wani hukunci a cikin daukaka karar da jam’iyyar Labour Party, LP, da dan takararta na gwamna, Ken Pela, Kotun Koli ta yi watsi da karar saboda rashin gaskiya da rashin cancanta.

Mai shari’a Musa Uwani Aba-Aji, wanda ya yanke hukuncin, ya ce karar ba ta da wani amfani domin wadanda suka shigar da karar ba za su iya tabbatar da ko daya daga cikin zarge-zargen nasu ba.

Daga bisani mai shari’a Aba-Aji ya yi watsi da karar gaba dayanta.

A halin da ake ciki dai, dukkan koke-koke guda uku da jam’iyyun APC, SDP da LP suka shigar, an yi watsi da su ne saboda rashin cancanta.

latest news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp