fidelitybank

Kotu ta tabbatar da kujerar gwamnan Binuwai

Date:

Kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen gwamnan jihar Benue da ke zamanta a Makurdi, ta tabbatar da nasarar gwamnan jihar Hyacinth Alia na jam’iyyar APC a zaɓen ranar 18 ga watan Maris.

Kotun ta yi watsi da karar da ɗan takarar jam’iyyar PDP, Titus Uba, ya shigar gabanta, inda yake kalubalantar sakamakon zaɓen.

Kotun ta ce ta kori ƙarar ne saboda ba ta da hurumin sauraron batun da aka kai mata.

Tawagar alƙalan kotun uku ƙarƙashin jagorancin mai shari’a, Ibrahim Karaye, sun bayyana cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar ne saboda abin da aka kai mata ya shafi batutuwa ne na gabanin zaɓe kamar yadda yake a sashe na 285 na dokar zaɓe.

Mista Titus na zargin Mista Alia da gabatar da takardar shaidar kammala karatu ta jabu a lokacin da ya tsaya takara.

Sai dai kotun ta ce a gaban hukumar zaɓe ta INEC ya kamata ya kai ƙorafinsa.

Sakamakon zaɓen da INEC ta fitar a wancan lokaci, ya nuna cewa Mista Alia ya samu nasara ne da kuri’u 473,933, inda ya doke takwaransa na PDP, Titus Uba, wanda ya samu kuri’u 223,913

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...
X whatsapp