Kotun ɗaukaka ƙara da ke zamanta a Abuja, a ranar Litinin ta tabbatar da zaben Gwamna Hyacinth Alia, na jam’iyyar APC a matsayin halastaccen gwamnan Benue.
Ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaben gwamna na ranar 18 ga watan Maris, Titus Uba ya garzaya kotun daukaka kara saboda bai gamsu da hukuncin karamar kotun da ta tabbatar da zaben Alia ba.
A kotun, Uba ya yi zargin cewa mataimakin Alia, Samuel Ode, ya gabatar da takardar shaidar jabu ga hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa kuma hakan ya saba wa sashe na 182(1)(j) na Tarayyar Najeriya, 1999 (da aka yi wa gyaran fuska).
Ya kuma yi ikirarin cewa an mika sunan Alia, a ƙasa da kwana 180 kafin ranar zaben, sannan Samuel Ode ba a miƙa shi ga hukumar zaɓe ba, bayan da jam’iyyar ta sake gudanar da zaben fidda gwani.
Kotun karkashin Mai shari’a Ibrahim Karaye, ta yi watsi da ƙarar a kan cewa lamarin ya kasance na kafin zaɓe.