fidelitybank

Kotu ta taƙa wa tsagin Gwamnan Bauchi na tsige shugaban PDP

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Zamfara ta ki amincewa da bukatar wani bangare mai goyon bayan shugaban kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP, Gwamna Bala Mohammed na gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa (NEC).

Kungiyar ta garzaya kotu domin ta ba da umarnin gudanar da taron na NEC yayin da rikicin bangaran jam’iyyar ya kara ruruwa.

Da yake yanke hukunci kan karar, Mai shari’a Salim Ibrahim ya ki amincewa da bukatar.

Wani bangare na jam’iyyar PDP a karkashin jagorancin gwamnan Bauchi Bala Mohammed, sun tunkari kotu suna neman a ba su umarnin gudanar da taron majalisar zartarwa ta kasa (NEC).

A baya dai wasu gwamnonin da aka zaba a jam’iyyar PDP karkashin jagorancin Mohammed sun yi yunkurin tsige shugaban riko na kasa Amb. Umar Damagum.

Matakin ya kara dagula rikicin cikin jam’iyyar, yayin da wasu masu ruwa da tsaki musamman masu biyayya ga ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike suka nuna adawa da matakin.

Ita ma babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin hana jam’iyyar cire Damagum.

An shigar da karar bangaren Mohammed ne a babbar kotun tarayya da ke jihar Zamfara.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp