Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki ta kasa da ta Jiha da ke zamanta a Lafiya, ta soke komawar Ovey John na Jamâiyyar PDP a matsayin zababben dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Keffi ta Gabas a Majalisar Jihar Nasarawa (NSHA).
Wannan hukuncin na zuwa ne bayan hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, ta bayyana Ovey John a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.
Kwamitin mai mutane uku karkashin jagorancin Mai shariâa Francisca Isong Nnang a lokacin da yake yanke hukuncin a ranar Lahadi a Lafiya, ya kammala da cewa INEC ta yi kuskure wajen ayyana dan takarar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben, inda ta yi watsi da Isah Adamu daga jamâiyyar APC.
Kotun ta yi bayanin cewa tazarar da Ovey ya jagoranta da ta samu kuriâu 1004, ta fadi kasa da adadin masu kada kuriâa da aka amince da su a rumfunan zabe hudu (4) da INEC ta soke zabe.
Don ci gaba da magance wannan sabani, kotun da Mai shariâa Francisca Isong Nnang ke jagoranta ta bayar da umarnin sake gudanar da zabe a runfunan zabe hudu da abin ya shafa, wato: Yarkade Primary School 003, Angwan Maiganga 014, Police Station 2 da Angwan Nepa dake cikin mazabar.