fidelitybank

Kotu ta soke kujerar Sanatan PDP a Nasarawa

Date:

Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki ta kasa da ta Jiha da ke zamanta a Lafiya, ta soke komawar Ovey John na Jam’iyyar PDP a matsayin zababben dan Majalisar Tarayya mai wakiltar mazabar Keffi ta Gabas a Majalisar Jihar Nasarawa (NSHA).

Wannan hukuncin na zuwa ne bayan hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, ta bayyana Ovey John a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

Kwamitin mai mutane uku karkashin jagorancin Mai shari’a Francisca Isong Nnang a lokacin da yake yanke hukuncin a ranar Lahadi a Lafiya, ya kammala da cewa INEC ta yi kuskure wajen ayyana dan takarar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben, inda ta yi watsi da Isah Adamu daga jam’iyyar APC.

Kotun ta yi bayanin cewa tazarar da Ovey ya jagoranta da ta samu kuri’u 1004, ta fadi kasa da adadin masu kada kuri’a da aka amince da su a rumfunan zabe hudu (4) da INEC ta soke zabe.

Don ci gaba da magance wannan sabani, kotun da Mai shari’a Francisca Isong Nnang ke jagoranta ta bayar da umarnin sake gudanar da zabe a runfunan zabe hudu da abin ya shafa, wato: Yarkade Primary School 003, Angwan Maiganga 014, Police Station 2 da Angwan Nepa dake cikin mazabar.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Ĉ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Ĉ™asa – Fadar Shugaban Ĉ˜asa

Fadar shugaban Ĉ™asa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan ĈŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun ShariÊĵar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban Ĉ™asa, Mohammed Namadi Sambo, ya Ĉ™aryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaĈ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta Ĉ™addamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Ĉ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaĈ™i...

Najeriya za ta kwashe Ĉ´an Ĉ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, Ĉ™asar...

Iran ta Ĉ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta Ĉ™addamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Ĉ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Ĉ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp