Alƙaliyar Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke tuhuma takwas daga cikin 15 da gwamnatin tarayya ke tuhumar madugun ‘yan aware na kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu.
Tuhume-tuhumen takwas na cikin laifukan da aka kara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa shugaban ‘yan awaren.
Yayin da take watsi da karar, Mai Shari’a Binta Nyako ta ce, zarge-zargen ba su bayyana laifin da wanda ake karar ya aikata ba.
Mai shari’ar ta ce, sato shugaban IPOB din da aka yi da manufar gudanar da bincike abu ne halastacce.
Ta kuma ce, da ma akwai umarnin kamu a kan Kanu bayan tserewa daga kasar a gaban kotu.
Sai dai lauyoyin da ke kare shi sun dage kan cewa, gwamnatin Najeriya ta karya dokar ƙasa da ƙasa tare da take hakkin Kanu, da sato shi daga wata ƙasar a bara.
Duk da cewa, har yanzu hukumomi ba su bayyana inda da kuma yadda aka kama Mista Kanu, kuma aka ta so ƙeyarsa ba, dangi da kuma lauyoyinsa na cewa, an kama shi ne a ƙasar Kenya cikin wani yanayi mai sarƙaƙiya.
Gwamnatin Kenya dai ta musanta wannan zargi. An ki ba da belin shugaban kungiyar ta IPOB a zaman na yau.
Ana zarginsa ne da ayukkan ta’addanci da kuma cin amanar ƙasa kuma yana fuskantar ɗaurin rai-da-rai idan aka same shi da laifi.