fidelitybank

Kotu ta sauke tuhuma 8 da gwamnati ke yi wa Nnamdi Kanu

Date:

Alƙaliyar Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke tuhuma takwas daga cikin 15 da gwamnatin tarayya ke tuhumar madugun ‘yan aware na kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu.

Tuhume-tuhumen takwas na cikin laifukan da aka kara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa shugaban ‘yan awaren.

Yayin da take watsi da karar, Mai Shari’a Binta Nyako ta ce, zarge-zargen ba su bayyana laifin da wanda ake karar ya aikata ba.

Mai shari’ar ta ce, sato shugaban IPOB din da aka yi da manufar gudanar da bincike abu ne halastacce.

Ta kuma ce, da ma akwai umarnin kamu a kan Kanu bayan tserewa daga kasar a gaban kotu.

Sai dai lauyoyin da ke kare shi sun dage kan cewa, gwamnatin Najeriya ta karya dokar ƙasa da ƙasa tare da take hakkin Kanu, da sato shi daga wata ƙasar a bara.

Duk da cewa, har yanzu hukumomi ba su bayyana inda da kuma yadda aka kama Mista Kanu, kuma aka ta so ƙeyarsa ba, dangi da kuma lauyoyinsa na cewa, an kama shi ne a ƙasar Kenya cikin wani yanayi mai sarƙaƙiya.

Gwamnatin Kenya dai ta musanta wannan zargi. An ki ba da belin shugaban kungiyar ta IPOB a zaman na yau.

Ana zarginsa ne da ayukkan ta’addanci da kuma cin amanar ƙasa kuma yana fuskantar ɗaurin rai-da-rai idan aka same shi da laifi.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp