fidelitybank

Kotu ta sassauta wa Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda wajen belin sa

Date:

Kotun Majistare ta jihar Kano mai lamba 58 karkashin jagorancin Aminu Gabari a ranar Alhamis ta yi nazari kan sharuddan belin da ta ayyana a baya kan Abdulmajid Sani Kwamanda.
Kadaura24 ta rawaito cewa, sakamakon rokon da lauyan Abdulmajid Danbilki kwamanda Barista Tajuddeen Funsho ya yi a gaban kotun.
Da yake gabatar da rokon, Barista. Funsho ya bukaci kotun da ta sake duba sharuddan da ta gindaya a baya a kan wanda yake karewa, inda ya ce wanda ake kara zai ci gaba da zuwa kotu, domin sauraren laifukan da ake kararsa akan su waÉ—anda suka shafi bata sunan gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
A martanin da ya mayar, lauyan masu shigar da kara, Barista. Wada Ahmad Wada, ya ce, batun sake duba belin, kotu ce ta yanke hukunci, inda ya yi fatan za a bi ka’idojin shari’a da adalci wajen sake nazarin.
A hukuncin da ya yanke, Alkalin kotun ya umurci Danbilki da ya gabatar da mutane 2 wadanda suka hada da: mahaifinsa ko wakilinsa, maimakon Wakilin Gabas na masarautar Kano da aka bukata tun da fari.
Hakazalika, kotun ta umurci wanda ake kara da ya gabatar da limamin na duk wani masallaci da ke unguwar Koki, ko kuma limamin kowane masallacin da ya ke gudanar da sallarsa a wajen.
Mai Shari’a Gabari ya kuma ba da umarnin cewa, haka nan wanda ake tuhuma zai iya kiran duk wani shugaban addini a cikin al’umma, idan har bai samu wani Imami da zai tsaya masa ba.
Wannan ya maye gurbin Babban Limamin Masallacin Hajiya Mariya Sanusi Dantata da ke unguwar koki da kotun ta ambata a baya.
Kotun ta dage zamanta zuwa ranar 19 ga Afrilu, 2023, domin ci gaba da ambato.

nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu É—auki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta É—aukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta É—aure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miÆ™a saÆ™on ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...
X whatsapp