Kotun Majistare ta jihar Kano mai lamba 58 karkashin jagorancin Aminu Gabari a ranar Alhamis ta yi nazari kan sharuddan belin da ta ayyana a baya kan Abdulmajid Sani Kwamanda.
Kadaura24 ta rawaito cewa, sakamakon rokon da lauyan Abdulmajid Danbilki kwamanda Barista Tajuddeen Funsho ya yi a gaban kotun.
Da yake gabatar da rokon, Barista. Funsho ya bukaci kotun da ta sake duba sharuddan da ta gindaya a baya a kan wanda yake karewa, inda ya ce wanda ake kara zai ci gaba da zuwa kotu, domin sauraren laifukan da ake kararsa akan su waÉ—anda suka shafi bata sunan gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje.
A martanin da ya mayar, lauyan masu shigar da kara, Barista. Wada Ahmad Wada, ya ce, batun sake duba belin, kotu ce ta yanke hukunci, inda ya yi fatan za a bi ka’idojin shari’a da adalci wajen sake nazarin.
A hukuncin da ya yanke, Alkalin kotun ya umurci Danbilki da ya gabatar da mutane 2 wadanda suka hada da: mahaifinsa ko wakilinsa, maimakon Wakilin Gabas na masarautar Kano da aka bukata tun da fari.
Hakazalika, kotun ta umurci wanda ake kara da ya gabatar da limamin na duk wani masallaci da ke unguwar Koki, ko kuma limamin kowane masallacin da ya ke gudanar da sallarsa a wajen.
Mai Shari’a Gabari ya kuma ba da umarnin cewa, haka nan wanda ake tuhuma zai iya kiran duk wani shugaban addini a cikin al’umma, idan har bai samu wani Imami da zai tsaya masa ba.
Wannan ya maye gurbin Babban Limamin Masallacin Hajiya Mariya Sanusi Dantata da ke unguwar koki da kotun ta ambata a baya.
Kotun ta dage zamanta zuwa ranar 19 ga Afrilu, 2023, domin ci gaba da ambato.