fidelitybank

Kotu ta samu dan Biden da laifi uku a Amurka

Date:

Kotun Amurka ta samu dan shugaban kasar Joe Biden, wato Hunter Biden, da laifin aikata manyan laifuka guda uku.

Zargin ya samo asali ne daga wani abin da ya faru a watan Oktoban 2018, lokacin da Hunter Biden ya sayi wata bindiga kirar revolver a wani shagon sayar da bindiga dake Delaware.

Bayan kimanin sa’o’i uku ana tattaunawa, alkalan kotun sun samu Hunter da laifin yin karya game da amfani da muggan kwayoyi da kuma mallakar bindiga.

Wannan hukuncin ya kasance wani lokaci mai tarihi domin shine karo na farko da aka samu dan gidan shugaban kasa da laifi, a lokacin mulkin mahaifinsa, duk da cewa laifin Hunter Biden ya faru ne kafin Joe Biden ya zama shugaban kasa.

Hunter Biden na fuskantar daurin shekaru 25 a gidan yari da kuma tarar dala 750,000 a lokacin yanke hukunci, duk da cewa a matsayinsa na mai laifin farko, akwai yuwuwar yanke masa hukunci kadan. Ana sa ran yanke hukunci a cikin kwanaki 120.

Masu gabatar da kara, karkashin jagorancin lauya na musamman David Weiss, y ace, ayyukan Hunter Biden, sun saba wa dokokin da ke nufin hana masu shan muggan kwayoyi tare da mallakar bindigogi.

Hukuncin ya kawo karshen wani babi na binciken da ma’aikatar shari’a ta yi kan Hunter Biden, wanda aka fara a shekarar 2018. Ana sa ran zai sake fuskantar wata shari’a a watan Satumba saboda laifukan haraji na tarayya.

Dukkan shari’o’in biyu David Weiss ne, wanda shugaba Trump ya nada a baya, wanda tawagarsa ta musanta wani dalili na siyasa da ke tattare da tuhumar.

Duk da hargitsin doka, Shugaba Biden da Fadar White House sun yi watsi da afuwa ga Hunter Biden.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp