Mai shari’a Ijeoma Ojukwu na babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Litinin ta samu babban mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara (SSA), Dr Doyin Okupe da laifin karbar kudi sama da naira miliyan 200 daga hannun tsohon mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Kanar Sambo Dasuki. .
Mai shari’a Ojukwu a hukuncin da ta yanke ya ce matakin da Okupe, wanda shi ne wanda ake kara na farko a karar da hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon-kasa ta EFCC ta shigar ya saba wa dokar satar kudi.
Yayin da yake bayyana cewa dokar ta tanadi cewa babu wani mutum ko wata kungiya da za ta karbi kudin da ya haura Naira miliyan 5 da miliyan 10 ba tare da wucewa ta wata cibiyar hada-hadar kudi ba, alkalin ya ce “babu wata shaida da ke nuna cewa kudaden sun bi ta wata cibiyar kudi”.
A cewar mai shari’a Ojukwu, hukumar NSA ba cibiyar hada-hadar kudi ba ce, inda ya kara da cewa ko da a ce shugaban kasa ne ya ba da izini bai ce dole a biya kudin a cikin tsabar kudi ba, wanda ya saba wa halasta kudaden haram.
Don haka kotun ta ce, “Na samu wanda ake kara na farko, Doyin Okupe da laifi a kirga 34, 35, 36…… 59.”