Wata babbar kotu a Abuja, ta yanke hukuncin kyale jam’iyyar APC mai mulkin Najeriya ta gudanar da babban taronta na kasa a ranar 26 ga watan Maris na wannan shekarar.
A ranar Juma’a alkalin kotun, Mai shari’a Bello kawu ya yanke hukunci cewa ‘ya’yan jam’iyyar ba su da hurumin kai kararta.
Ya ce wani umarnin Kotun Kolin Najeriya kan wani batu irin wannan ya sha gaban wanda babbar kotun ta fitar na 18 ga watan Nuwambar bara.
Kotun ta daga zamanta zuwa ranar 30 ga wannan watan na Maris domin ci gaba da sauraren karar.
Wani mamba a jam’iyyar mai suna, Salisu Umaru ne ya shigar da kara inda yake so kotun ta hana jam’iyyar ta APC da gwamna Mai Mala Buni da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, INEC su shirya babban taro na kasa na jam’iyyar har sai bayan an kammala sauraren karar da ya shigar.