fidelitybank

Kotu ta sa a tsare ɗan Kano da ya yi Burutai ƙazafi

Date:

Wata babbar kotu a jihar Kano, ta gurfanar da wani Ibrahim Khalil Danshagamu, mai fafutukar yada labaran yanar gizo, bisa samunsa da laifin bata sunan tsohon babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai mai ritaya.

Mai shari’a Halima A.B ta jagoranta ta tasa keyar sa. Danshagamu wanda ake kara dai an gurfanar da shi a gaban Kotu, bisa zarginsa da yada wani faifan bidiyo a shafukansa na sada zumunta, inda ya yi ikirarin cewa, Buratai ya gina gidajen mai sama da 60 a Kano daga cikin kudin sayen makamai.

Tsohon Jakadan Najeriya a Jamhuriyar Benin (Buratai), ya bukaci ‘yan sanda da su kamo wanda ake tuhuma don tabbatar da ikirarin.

Danshagamu wanda ake tuhuma ya musanta tuhumar da ake yi masa bayan da ‘yan sanda suka kama shi.

Lauyan wanda ake kara, Barista S.A Abdullahi, ya roki kotu da ta bayar da belin wanda yake karewa, amma alkalin kotun ya ki amincewa da hakan, saboda laifin da ake tuhumar ya saba wa sashi na 371 da 115, saboda laifin da ake tuhumar zai kai ga daurin shekaru uku a gidan yari.

Don haka alkalin ya ba da umarnin a aika wanda ake kara zuwa ga likitan hauka na jihar don tantance ko yana cikin ma’anarsa a lokacin da ya raba faifan bidiyon.

Lauyan wanda ya shigar da karar Barista Hussaini Makari, a lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan zaman kotun, ya bayyana cewa, wanda yake karewa ya kuma jefa kalubalen cewa, a shirye yake ya janye karar da ake tuhumar wanda ake kara idan har wani dan jihar Kano zai iya nuna wani abu.

bbc news nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...
X whatsapp