fidelitybank

Kotu ta sa a kamo Dan Birtaniya ma yunkurin kifar da Tinubu daga mulki

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, ta bayar da sammacin kama ɗan ƙasar Birtaniya, Andrew Wynne tare da wasu ‘yan Najeriya bisa zargin cin amanar ƙasa da ta’addanci a lokacin zanga-zangar adawa da yunwa da tsadar rayuwa.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mai shari’a Emeka Nwite ne ya bayar da sammacin bayan ƙarar da babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya shigar gaban kotun.

Sufeton ‘yansandan ya zargi zargi Wynne da wasu ƴan zanga-zangar 10 da aka tsare da laifin haɗin baki do nufin hamɓarar da shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu, da cin amanar ƙasa da tayar da zaune tsaye, da kuma ta’addanci, wanda ya saɓa wa sassa da dama na dokar ƙasa.

Waɗanda ake tuhuman, ana kuma zarginsu da hannu wajen shirya kai hare-hare da suka haɗa da ƙona harabar babbar kotu da ofishin NCC, da kuma gidan buga takardu a Kano.

A farkon wannan makon ne dai rundunar ‘yansandan Najeriya ta ayyana neman mista Wynne ruwa a jallo, bisa waɗannan zarge.

To sai a cikin wata hira da ya yi da gidan talbijin na Channels Mista Wynne, ya musanta zarge-zargen tare da cewa zai amsa gayyatar ‘yansanda ta manhajar Zoom ko whatsapp.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp