Babban kwamandan hukumar Hisbah ta jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurwa, ya tabbatar da cewa an kulle dukkan asusun bankin na hukumar, biyo bayan karar da masu otal a jihar suka shigar da hukumar.
Jamiāan Hisbah sun kai samame a Otal-otal da wuraren shakatawa da sauran wuraren nishadi a Kano da nufin tsarkake jihar daga munanan dabiāu da munanan ayyuka.
Daurawa ya ce, āEh, gaskiya duk an kulle asusun bankin mu. Na aika da wakili ya gana da babban lauya saboda ba a fada mana laifin da ake zarginsa da kuma dalilin rufe asusun ba.
Mun samu takardan kotu da ke nuna rashin daāa a wasu otal guda biyu, wanda hakan ya sa aka tuhumi N700,000 da N100,000, bi da bi. Takardar ta bukaci a hada su a biya su Naira 800,000 wanda hakan ya sa aka rufe asusun mu.
āYa kamata a gaya mana laifin da muka aikata domin mu nemi lauyoyinmu su shiga cikin tattaunawar. Idan muka kasa kare kanmu, to za a hukunta mu.ā urawa ya kuma nuna damuwarsa kan yadda hukuncin da kotun ta yanke ya gurgunta ayyukan Hisbah saboda takaita asusun ajiyar banki.