fidelitybank

Kotu ta nemi El-Rufai ya biya diyyar miliyan 900 kan tsare wasu Dattawa

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Kaduna ta yanke hukunci inda ta nemi tsohon gwamnan Jihar, Nasir El-Rufai, da wasu mutum biyar su biya diyyar naira miliyan 900 a matsayin diyyar tsare wasu dattawan Adara da ke ƙaramar hukuma Kajuru a jihar ba bisa ƙa’ida ba a shekarar 2019 a ƙaramar hukumar Kajuru.

Gidan talbijin na Channels wanda ya rawaito labarin ya ce mai shari’a Hauwa’u Buhari ce ta yanke hukuncin a kan ƙarar da Awemi Dio Maisamari da wasu dattawan Adara takwas suka shigar, inda kotu ta tabbatar da cewa an tsare su ne bisa zargin hannu a kisan sarkin gargajiyarsu, Raphael Maiwada Galadima, ba tare da wani dalilin doka ba.

Kotu ta ce El-Rufai ya ci gaba da matsa lamba a kan a kama su, kuma ya aikata hakan ne ba a matsayinsa na gwamna ba.

Kotu ta yi watsi da korafe-korafen da waɗanda ake ƙara suka gabatar.

Lauyar da ta wakilci masu ƙarar, Gloria Ballason, ta bayyana hukuncin a matsayin babbar nasara a yaƙi da cin zarafin da gwamnoni da shugabanni ke yi da amfani da karfi da ikon da ke hannunsu.

Dattawan takwas, ciki har da tsohon kwamishina na ƴan sanda mai ritaya, an kama su ne a wani taron al’umma da El-Rufai ya shirya a shekarar 2019, bayan sace da kashe sarkinsu.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp