fidelitybank

Kotu ta nemi El-Rufai ya biya diyyar miliyan 900 kan tsare wasu Dattawa

Date:

Wata babbar kotun tarayya da ke Kaduna ta yanke hukunci inda ta nemi tsohon gwamnan Jihar, Nasir El-Rufai, da wasu mutum biyar su biya diyyar naira miliyan 900 a matsayin diyyar tsare wasu dattawan Adara da ke ƙaramar hukuma Kajuru a jihar ba bisa ƙa’ida ba a shekarar 2019 a ƙaramar hukumar Kajuru.

Gidan talbijin na Channels wanda ya rawaito labarin ya ce mai shari’a Hauwa’u Buhari ce ta yanke hukuncin a kan ƙarar da Awemi Dio Maisamari da wasu dattawan Adara takwas suka shigar, inda kotu ta tabbatar da cewa an tsare su ne bisa zargin hannu a kisan sarkin gargajiyarsu, Raphael Maiwada Galadima, ba tare da wani dalilin doka ba.

Kotu ta ce El-Rufai ya ci gaba da matsa lamba a kan a kama su, kuma ya aikata hakan ne ba a matsayinsa na gwamna ba.

Kotu ta yi watsi da korafe-korafen da waɗanda ake ƙara suka gabatar.

Lauyar da ta wakilci masu ƙarar, Gloria Ballason, ta bayyana hukuncin a matsayin babbar nasara a yaƙi da cin zarafin da gwamnoni da shugabanni ke yi da amfani da karfi da ikon da ke hannunsu.

Dattawan takwas, ciki har da tsohon kwamishina na ƴan sanda mai ritaya, an kama su ne a wani taron al’umma da El-Rufai ya shirya a shekarar 2019, bayan sace da kashe sarkinsu.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp