Wata babbar kotun tarayya da ke Kaduna ta yanke hukunci inda ta nemi tsohon gwamnan Jihar, Nasir El-Rufai, da wasu mutum biyar su biya diyyar naira miliyan 900 a matsayin diyyar tsare wasu dattawan Adara da ke ƙaramar hukuma Kajuru a jihar ba bisa ƙa’ida ba a shekarar 2019 a ƙaramar hukumar Kajuru.
Gidan talbijin na Channels wanda ya rawaito labarin ya ce mai shari’a Hauwa’u Buhari ce ta yanke hukuncin a kan ƙarar da Awemi Dio Maisamari da wasu dattawan Adara takwas suka shigar, inda kotu ta tabbatar da cewa an tsare su ne bisa zargin hannu a kisan sarkin gargajiyarsu, Raphael Maiwada Galadima, ba tare da wani dalilin doka ba.
Kotu ta ce El-Rufai ya ci gaba da matsa lamba a kan a kama su, kuma ya aikata hakan ne ba a matsayinsa na gwamna ba.
Kotu ta yi watsi da korafe-korafen da waɗanda ake ƙara suka gabatar.
Lauyar da ta wakilci masu ƙarar, Gloria Ballason, ta bayyana hukuncin a matsayin babbar nasara a yaƙi da cin zarafin da gwamnoni da shugabanni ke yi da amfani da karfi da ikon da ke hannunsu.
Dattawan takwas, ciki har da tsohon kwamishina na ƴan sanda mai ritaya, an kama su ne a wani taron al’umma da El-Rufai ya shirya a shekarar 2019, bayan sace da kashe sarkinsu.