Kotun sojin Myanmar ta yankewa tsohuwar shugabar kasar Aung San Suu Kyi, karin daurin shekara uku a gidan kaso kan laifin magudin zabe, kamar yadda lauyanta ya shaidawa BBC.
Ms Suu Kyi dai na zaman kason daurin shekara 20 kan laifuka 11 da ake zarginta da shi, har ma da wasu karin laifukan da ba a kai yin shari’arsu ba.
Ta musanta dukkan zarge-zargen da akai mata, a shari’ar da masu rajin kare hakkin dan adam sukai allawadai da zargin gwamnatin soji da yi ma ta bita da kullin siyasa.
Lauyan tsohuwar shugabar, ya ce cikin sabon hukuncin da aka yanke mata har da aiki mai tsananin gaske.
Suu Kyi mai shekara 76 da ta taba daukar lambar yabo ta Nobel, ta shafe yawancin rayuwarta karkashin daurin talala a babban birnin kasar Nay Pyi Taw.
Sojojin Myanmar din sun hana mutane da ‘yan jarida damar shiga kotun a lokacin da ake yanke hukuncin, an kuma hana hatta lauyoyin ta ba a ba su damar magana da ‘yan jarida ba.
Ms Suu Kyi da yawancin mambobin jam’iyyar ta na daga cikin sama da mutum 15,000 da gwamnatin sojin da ta yi juyin mulki a Myanmar ta daure tun bayan karbe kasar.
Har yanzu mutum 12,000 na gidan kaso daban-daban da ke Burma.