fidelitybank

Kotu ta kori shugaban hukumar wasanni na Taraba

Date:

Rikicin shugabanci da ya dabaibaye hukumar kwallon kafa ta jihar Taraba (FA), ya dauki sabon salo.

Wannan na zuwa ne yayin da wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Jalingo, babban birnin jihar, ta kori shugaban da ke kan karagar mulki, Timothy Heman.

Alkalin kotun, Mai shari’a Simone Amobeda ya bayar da umarnin a gaggauta rantsar da wanda ya shigar da kara, Sanusi Mahmoud a matsayin shugaban kungiyar a jihar.

Rikicin, wanda aka shafe shekaru uku ana yi, ya yi illa ga harkar kwallon kafa a Jihar.

Alkalin ya gargadi shugaban mai ci da cewa cikin gaggawa ya daina bayyana kansa a matsayin shugaban hukumar FA ta jihar.

Kotun ta kuma umarci kungiyar a matakin kasa da ta daina hulda da shugaban da ke kan karagar mulki.

Da yake jin dadin sakamakon hukuncin, lauyan Mahmoud Isa Buba, ya bukaci wadanda suka yi korafin su hada kai da Mahmoud domin ciyar da kwallon kafa gaba a Taraba.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp