Kotun sauraren kararrakin zabe ta jiha, ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Filato, Moses Sule.
Kotun sauraren kararrakin zabe da ke zamanta a Jos, ta kori dan majalisar, wanda aka zaba a jamâiyyar Peoples Democratic Party, PDP a zaben da ya gabata.
An sauke shi ne tare da Danjuma Azi, mamba mai wakiltar mazabar Jos ta Arewa maso yamma a majalisar
Kotun ta bayyana tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar, Hon. Naanlong Daniel and Hon. Mark Naâah, dukkan jamâiyyar APC ne a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.
Mai shigar da karar ya kalubalanci daukar nauyin Sule da Azi ne bisa hujjar cewa PDP ba ta cancanci shiga zaben ba saboda rashin tsarin jamâiyya.
Da take yanke hukuncin, kotun karkashin jagorancin Muhammad Tukur ta ce PDP ba ta cancanci daukar nauyin wadanda aka kara a zaben ba.
Ya ce kasancewar jam’iyyar ba ta da tsari, “babu wani abu da zai iya tsayawa kan komai”.