Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta kori Chijioke Edeoga a matsayin dan takarar gwamna na jamâiyyar Labour a jihar Enugu.
Ku tuna cewa Evarest Nnaji, wanda aka fi sani da Odengene ya garzaya kotun Abuja domin kalubalantar zaben fidda gwani da aka gudanar a watan Mayu wanda ya samar da Chijioke a matsayin dan takarar jamâiyyar.
Mai shariâa Evelyn Maha wacce ta yi watsi da zaben fidda gwanin ta umurci jamâiyyar ta gudanar da sabon zaben fidda gwani a cikin kwanaki 14.
Mutanen biyu dai âyaâyan jamâiyyar PDP ne amma a farkon shekarar sun sauya sheka ne domin fafatawar neman tikitin jamâiyyar LP na zaben gwamna mai zuwa.