fidelitybank

Kotu ta kakabawa Murja ‘Yar TikTok takunkumi

Date:

Wata babbar kotu da ke Kano ta ba da belin fitacciyar jarumar Tiktok, Murja Ibrahim Kunya a kan kuɗi naira dubu 500 da kuma gabatar da mutum biyu da za su tsaya mata.

Baba Jibo Ibrahim, mai magana da yawun kotunan Kano ya tabbatar wa BBC wannan labarin, inda ya ce kotun ta ba da belin Murja ne bayan zaman kotun da aka yi a yau Litinin.

Alƙalin ya ce dole ne ɗaya daga cikin masu tsaya mata ya zama ɗan’uwanta na jini, sannan ɗayan kuma dole ne ya zama yana da shaidar mallakar fili a Kano.

Alƙali Nasiru Saminu ya kuma ce ya bayar da belinta ne bisa hujjar cewa matashiyar ‘yar Tiktok din ta wuce kwana 30 a garƙame.

Sai dai alƙalin ya haramta wa jarumar tiktok ɗin amfani da shafukan sada zumunta har zuwa lokacin kammala shari’ar.

Alƙalin ya kuma ce kwamishinan ƴansanda na da ikon sake kama Murja matuƙar ta ƙi mutunta umarnin haramta mata amfani da shafukan sada zumuntar tare da gabatar da ita gaban kotu.

Mai shari’ar ya ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 16 ga watan Mayu don ci gaba da zama a kan shari’ar.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp