fidelitybank

Kotu ta jingine dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Kano ta dakatar da shugabannin jam’iyyar APC a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa daga ɗaukan ƙarin mataki a kan dakatar da shugaban jam’iyyar ta ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

A wata takardar kotu mai ɗauke da sa hannun magatakardan kotun, Usama Ibrahim Isah, mai shari’ar Abdullahi Muhammad Liman ne ya bayar da umarnin inda ya buƙaci mutanen da ake ƙara da su guji aiwatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje har zuwa lokacin da za a saurari ƙarar da shugaban APC ya shigar a kotu.

Umarnin kotun ya zo ne sa’oi bayan da babbar kotu a Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje saboda zarginsa da rashawa.

Kotun ta kuma umarci ɓangarorin da su tsaya kan matsayin da ake kafin taron manyan jam’iyyun APC na mazaɓar ta Ganduje wanda bayansa ne aka dakatar da shugaban jam’iyyar a mazaɓar. In ji BBC

Mai shari’a Liman ya sa ranar 30 ga watan Afrilu a matsayin ranar da za a saurari shari’ar.

Waɗanda ake ƙara sune Haladu Gwanjo da Nalami Mai AC da Muhammadu Baiti da Danmalam Gata da Musa Lado da Laminu Sani Barguna da Umar Sanda da Auwalu Galadima da Abubakar Daudu.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp