fidelitybank

Kotu ta jingine dakatarwar da aka yi wa Ganduje daga APC

Date:

Wata babbar kotun tarayya a Kano ta dakatar da shugabannin jam’iyyar APC a mazaɓar Ganduje a ƙaramar hukumar Dawakin Tofa daga ɗaukan ƙarin mataki a kan dakatar da shugaban jam’iyyar ta ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

A wata takardar kotu mai ɗauke da sa hannun magatakardan kotun, Usama Ibrahim Isah, mai shari’ar Abdullahi Muhammad Liman ne ya bayar da umarnin inda ya buƙaci mutanen da ake ƙara da su guji aiwatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje har zuwa lokacin da za a saurari ƙarar da shugaban APC ya shigar a kotu.

Umarnin kotun ya zo ne sa’oi bayan da babbar kotu a Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Ganduje saboda zarginsa da rashawa.

Kotun ta kuma umarci ɓangarorin da su tsaya kan matsayin da ake kafin taron manyan jam’iyyun APC na mazaɓar ta Ganduje wanda bayansa ne aka dakatar da shugaban jam’iyyar a mazaɓar. In ji BBC

Mai shari’a Liman ya sa ranar 30 ga watan Afrilu a matsayin ranar da za a saurari shari’ar.

Waɗanda ake ƙara sune Haladu Gwanjo da Nalami Mai AC da Muhammadu Baiti da Danmalam Gata da Musa Lado da Laminu Sani Barguna da Umar Sanda da Auwalu Galadima da Abubakar Daudu.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp