fidelitybank

Kotu ta hana PDP tsige shugaban ta Damagun

Date:

Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta dakatar da kwamitin amintattu BOT da majalisar ƙolinta daga cire Umar Damagun a matsayin shugaban riƙo na jam’iyyar.

Mai shari’a Peter Lifu ne ya bayar da umarnin a hukuncin da ya yanke, inda ya ce Damagun ne zai cigaba da zama shugaban jam’iyyar na riƙo har zuwa ranar da za a gudanar da babban taron jam’iyyar a watan Disamban 2025.

Alƙalin ya ce bisa la’akari da sashe na 42 da 47 da 67 na jam’iyyar, a babban taron jam’iyyar ne kawai za a zaɓan wani sabon shugaba, inda ya ce dole duk wani ɗan jam’iyyar ya yi biyayya ga kundin tsarin mulkin jam’iyyar.

Mai shari’a Lifu ya ƙara da cewa yanzu zangon shugabancin PDP na Arewa ne, inda ya ƙara da cewa tunda an zaɓi Damagun ne domin ƙarasa zangon mulkin Iyorchia Ayu wanda shi ma ɗan yankin ne, dole ya ƙarasa zangon.

legit breaking news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp