Wata babbar kotu da ke zamanta a Kwale, jihar Delta, ta hana Babban Bankin Najeriya (CBN) da Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) dakatar da Godwin Emefiele na takarar shugaban kasa.
Emefiele dai ya garzaya kotu ne domin samun izini da za ta ba shi damar ci gaba da zama a matsayin gwamnan CBN a yayin da ya ke neman takarar shugaban kasa.
An tattaro a ranar Juma’a cewa, kotu ta ba da umarnin hana bankin da INEC yin wani yunkuri na dakatar da Emefiele na takarar shugaban kasa a 2023.
A cewar rahoton jaridar Punch, an shigar da bukatar a asirce ne a ranar 5 ga watan Mayu, sannan aka yanke hukunci a ranar 12 ga watan Mayu.