Babbar Kotun Taraiya a Abuja ta yi watsi da roƙon belin da a ka shigar wajen ta na dakataccen Mataimakin Kwamishinan Ƴan Sanda, Abba Kyari.
Da ya ke yanke ƙwarya-ƙwaryan hukunci a kan roƙon belin, Mai Shari’a Inyang Ekwo, ya ce hakan ba zai yiwu ba sabo da akwai umarnin da wata kotu ta bayar na cewa Hukumar Yaƙi da sha da Fataucin Ƙwayoyi ta Ƙasa, NDLEA ta tsare Kyari tsawon kwanaki 14 domin ta samu ta kammala bincikenta.
Ekwo ya ƙara da cewa kotun, wacce ta bada umarnin NDLEA ta ci gaba da tsare Kyari, ta na da cikakken hurumi na yin hakan.
Ya ƙara da cewa sai waɗannan kwanaki 14 ɗin sun cika sannan zai saurari ƙarar da Kyari ya shigar ta take masa haƙƙinsa.
Alkalin ya dage zaman sai ranar 15 ga watan Maris domin sauraren ƙarar 5a Kyari.